Gwamna Badaru Abubakar ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan marigayi tsohan shugaban karamar hukumar Miga
Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya aike da sakon taaziyya ga iyalan marigayi tsohan shugaban Karamar Hukumar Miga Alhaji Muhammad Sabi’u Miga
Sakon taaziyyar mai dauke da sa hannun mai bawa gwamnan shawara kan yan jaridu da hulda da jama-a Habibu Nuhu Kila, gwamnan ya bayyana rasuwar marigayi a matsayin babban rashi ga iyalai da kuma sauran alummar musulmi
Inda kuma ya yi adduar Allah ya ji kansa ya kuma baiwa iyalai da yan uwa hakurin jure babban rashin da aka yi