

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Gwamna Muhammad Badaru Abubakar na jihar Jigawa ya aike da sakon ta’aziyya ga mai martaba sarkin Kazaure Alhaji Najib Hussaini Adamu bisa rasuwar Tafidan Kazaure Alhaji Iliyasu Adamu.
A sakon ta’aziyyar mai dauke da sa hannun mai bashi shawara kan kafafan yada labarai da hulda da jama’a, Habibu Nuhu Kila, gwamnan ya bayyana rasuwar marigayin a matsayin babban rashi ba ga masarautar Kazaure ko jihar Jigawa kadai ba, har ma ga kasarnan baki daya da kuma sauran alummar musulmi.
Gwamnan ya kuma bayyana marigayi Tafidan Kazaure Alhaji Iliyasu Adamu a matsayin gogaggen ma’aikaci, shugaban al’umma da ya himmatu wajen yiwa al’umma hidima da kuma kawo sauye sauye ga al’umma.
Daga nan sai ya yi adduar Allah ya ji kansa ya kuma baiwa iyalai da ‘yan’uwa hakurin jure rashinsa.