Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce zata kirkiri Makarantun Makiyaya Mata da nufin koya musu Sana’oin hannu a sassan Jihar nan.
Sakatariyar Zartarwa ta hukumar Ilimin Makiyaya ta Jihar Jigawa Hajiya Ramatu Muhammad, ita ce ta bayyana hakan a lokacin da take tattaunawa da manema labarai a Ofishin ta dake Dutse.