Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da nuna wasu manyan fina-finai masu dogon zango 22 sakamakon zarginsu da saɓa ƙa’idar hukumar.
Cikin wata sanarwa da jami’in hul da jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar ya ce shugaban hukumar Abba Al-Mustapha ne bayar da umarcin saboda a cewarsa masu shirya fina-finan sun saɓa ƙa’idojin hukumar waɗanda suka tanadi cewa dole ne hukumar ta tace su kafin fitar da su.
Wasu daga cikin fina-finan da dakatarwa ta shafa sun haɗa da
- Dadin Kowa
- Labarina
- Gidan Sarauta
- Manyan Mata
- Dakin Amarya
- Kishiyata
- Garwashi
- Jamilun Jiddan
- Mashahuri
- Wasiyya
- Tawakkaltu
- Mijina
- Wani Zamani
- Mallaka
- Kudin Ruwa
- Boka Ko Malam
- Wayasan Gobe
- Rana Dubu
- Fatake
- Shahadar Nabila
- Tabarmar
- Rigar Aro