

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Ministar kudi, kasafi da tsare-tsare Zainab Ahmed Shamsuna, tace gwamnatin tarayya bata da wani kuduri na rage yawan ma’aikatan gwamanati a fadin kasar nan.
Zainab Shamsuna ta bayyan haka ne a cikin shirin barka da Safiya na gidan talabijin na kasa NTA da safiyar yau alhamis.
Ministar ta musanta rade-radin da ke yawo cewa gwamanati na shirin korar ma’aikata daga aiki domin rage barnatar kudade.
Tace shugaban kasa Buhari ya nanata cewa baza’a kori kowa ba, haka kuma ministan tace gwamnati tana bawa mutane Kwarin guiwar tsayawa da kafarsu maimakon Dogara da aikin gwamnati, ta hanyar basu basussuka da tallafi.
Zainab Shamsuna tace gwamnati taza rage kashe kudade domin cimma burukan da aka sanya agaba da kuma cigaba da tafiya da sauran hakumomi a kasar nan.
Kazalika tace shugaban kasa ba shida burin ragewa maaikata lokacin aiki, wanda ake bashi shawara tun farkon hawansa kugerar mulkin kasar nan.
Haka kuma ministar tayi tawassali da cewa shugaba Muhammadu buhari bai taba kin biyan albashi, ko fansho ba.