

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da cire harajin Naira 10 ga kowace lita a kan duk wani abin sha da baya dauke da sinadarin barasa, da kuma masu zaki.
Wannan din dai a matsayin wani nau’in haraji da aka sanya akan izinin samarwa, da izini da siyar da kaya.
Ministar kudi, kasafi da tsare-tsare ta kasa, Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a yayin gabatar da kasafin kudin shekarar 2022 ga jama’a jiya Laraba a Abuja.
A cewarta, sabuwar manufar da aka bullo da ita tana cikin dokar kudi da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya wa hannu a ranar 31 ga watan Disamba, 2021 ta bara.
Har ila yau, ministar ta ce gwamnati ta bullo da wata doka da ta bukaci kamfanonin kasashen waje da ke kasuwanci a kasar nan su karba tare da mika haraji ga Hukumar Harajin Cikin Gida ta Tarayya.
A cewarta, sabuwar manufar tana kuma kunshe ne a sashe na 30 na dokar kudi da ta yi wa tanadin sashe na 10, 31 da 14 na harajin ga kamfanonin yanar gizo da ba na kasar nan ba.