Gwamnatin Tarayya tace ta fito da wasu lambobi na komfuta domin maye gurbin takardar shaidar zama ɗan ƙasa

0 165

Gwamnatin Tarayya tace ta fito da wasu lambobi na komfuta domin maye gurbin takardar shaidar zama dan kasa.

Ministan sadarwa da tattalin arzikin komfuta, Isa Ali Pantami, ya fadi haka a wani taron karawa juna sani akan canja lambar shaidar zama dan kasa, wanda hukumar shaidar zama dan kasa ta shirya a Abuja.

Yace gwamnati ta amince da fasahar domin tabbatar da tsaron sirrikan mutane da bayanansu, da kuma rage yawaitar samun lambar zama dan kasa ba bisa ka’ida ba.

Ministan wanda ya samu wakilcin darakta janar na hukumar shaidar zama dan kasa, Aliyu Abubakar, yace za a fara amfani da sabbin lambobin daga ranar 1 ga watan Janairun da za mu shiga.

Aliyu Abubakar yace manufar shirin shine tattaunawa kafada da kafada da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da fahimtar lambar.

Leave a Reply

%d bloggers like this: