Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta gargadi al’ummar Musulmi da su guji kin yin azumin watan Ramadan da gangan

0 58

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta gargadi al’ummar Musulmi da su guji kin yin azumin watan Ramadan da gangan.

A wani sakon murya ta WhatsApp da ya aika wa kungiyoyin yada labarai a Kano, kwamandan hukumar Hisbah na jihar, Haroun Ibn-Sina, ya ce hukumar ba za ta kyale duk wanda aka samu yana cin abinci da rana ba tare da wani kwakwakwaran dalili ba.

A cewarsa, hukumar Hisbah ba za ta nade hannunta tana ganin yadda matasa musulmi ke keta hurumin addinin Musulunci a jihar ba, musamman a wannan wata mai alfarma, inda ake bukatar musulmi su gudanar da cikakkiyar ibada ga Allah.

Haruna Ibn-Sina ya kara da cewa, hukumar Hisbah ba za tayi kasa a gwiwa ba, wajen gudanar da aikinta na tabbatar da cikakken bin tsarin shari’ar Musulunci a cikin watan Ramadan da ma bayansa, inda ya ce duk wanda aka samu yana saba wa Shari’a, za a hukunta shi.

Haruna Ibn-Sina ya jaddada cewa Hisbah ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na yaki da badala a Kano.

Leave a Reply

%d bloggers like this: