Hukumar NCDC ta sanar da sabbin mutane 573 da suka harbu da cutar Corona

0 58

Cibiyar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Kasa NCDC ta sanar da sabbin mutane 573 da suka harbu da cutar Corona a kasa baki daya.

NCDC ta sanar da cewa mutanen sun fito ne daga Jihohi 7 na kasar nan.

Cibiyar ta ce Lagos (281), Benue (202), Kano (61), Borno (20), Jigawa (5), Edo (2), and Oyo (2)

NCDC ta kuma ce mutane 572 ne aka sallame su a jiya daga cibiyoyin kula da masu cutar, wanda hakan ya ke nuni da cewa kimanin mutane dubu 215 da 39 ne suka warke daga cutar a kasa baki daya.

Haka kuma an bada rahotan cewa Mutane 3 ne cutar Corona ta hallaka a jiya wanda hakan ya kawo adadin mutanen da cutar ta kashe zuwa dubu 3 da 39.

Kazalika, an bada rahotan cewa kimanin mutane dubu 243 da 450 ne suka harbu da cutar tun bayan bayyanarta a jihohi 36 ciki harda birnin tarayya Abuja.

Leave a Reply

%d bloggers like this: