

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta ce duba matsalolin da aka fuskanta yayin zaben 2019 da ya gabata zai taimaka wajen samun gyare gyare a babban zaben 2023 dake tafe.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar Mr. Fetus Okoye ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kaduna, inda ya ce duba matsalolin da aka fuskanta yayin zabe 2019 zai taimaka matuka wajen tunkarar zaben 2023.

Okoye ya ce hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa zata yi aiki da majalisar dattawa domin samun managartan tsare tsare akan zaben dake tafe cikin 2023.
Ya kara da cewa hukumar har ila yau tana duba rahoton da masu sa ido kan zabe na cikin gida da kuma na kasashen waje suka gabatar kan zaben 2019.