Jam’iyyar PDP ta yi Allah-wadai da manufar rufe iyakokin kasar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi..
Shugaban kwamitin yakin neman zaben gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Jigawa, Alhaji Isa Duniya Bahutu ne, ya bayyana hakan jiya a taron tuntubar jam’iyyar PDP da aka gudanar a karamar hukumar Yankwashi.
Ya zargi jami’an kwastam da laifin kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, sakamakon sintiri na baya-bayan nan a kan iyakar Babura da Jamhuriyyar Nijar.
Ya yi kira ga masu kada kuri’a akan su koya wa jam’iyyar APC darasi na siyasa ta hanyar kin amincewa da ita a zaben 2023.
Tun da farko dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Alhaji Mustapha Sule Lamido ya zargi gwamnatin jihar Jigawa da cire tsofaffi daga dukkanin ayyukan kiwon lafiya na jihar.