

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Asusun kula da kananan yara na majalisar dinkin duniya ya bayyana damuwa bisa yadda kididdiga ke nuna cewa adadin yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya ya kai miliyan 18 da rabi, kuma yana ci gaba da hauhawa.
Shugaban asusun a jihar Kano, Rahama Farah, wanda ya bayana haka a wata tattaunawa da ‘yan jarida a kan shirin ilimin ‘yaya mata ya ce daga cikin yara miliyan 18 da dubu dari 5 din, miliyan 10 mata ne, wanda yake a mastayin kaso 60 na ilahirin adadin.
Ya bayyana damuwa a kan yadda kididdigar ta ta’azzara rashin daidaito a tsakanin jinsi, inda yarinya daya cikin ‘yaya mata 4 daga iyalan da basu da karfin tattalin arziki a yankunan karkara ne kawai suka kammala karamar sakandire.
Farah ya ce hare hare da ake kai wa makarantu da wasu cibiyoyin ilimi sun taimaka wajen rage rage dauki da yara ke yin a neman ilimi a fadin kasar, inda yace akwai yiwuwar hakan ya shafi karin ‘yaya mata fiye da maza.
Sai dai ya ce kawo dauki da asusun kula da kananan yara tare da gwamnati da sauran kungiyoyi suka yi, ya sa yanzu yara mata miliyan 1 da dubu dari 4 sun yi samu damar komawa makaranta.