Kananan hukumomi guda 2 ne suke karkashin ikon kungiyar Boko Haram – Zulum

0 77

Gwamna Babangana Zulum na jihar Borno ya sanar da cewa kananan hukumomin jihar guda 2 suna karkashin ikon kungiyar Boko Haram.

Kananan hukumomin sune Abadam da Guzamala.

Gwamnan ya sanar da haka lokacin da yake zantawa da ‘yan kwamitin sojoji na majalisar dattawa, wadanda suka kai masa ziyarar ban girma yau a gidan gwamnati dake Maiduguri.

Babagana Zulum ya bayyana damuwa bisa samuwar ‘yan kungiyar ISWAP a kudancin jihar ta Borno.

Leave a Reply

%d bloggers like this: