Karamar Hukumar Kafin Hausa ta kafa kwamiti domin yin sintirin hana fulanin Udawa lalata kayayyakin amfanin gona

0 72

Karamar Hukumar Kafin Hausa ta kafa kwamiti domin yin sintirin hana fulanin Udawa lalata kayayyakin amfanin gona da nufin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin

Shugaban KH Alhaji Muhammad Saminu Yahaya ya bayyana hakan a lokacin kaddamar da kwamitin, inda ya bukaci yan kwamitin su gudanar da aikinsu bil hakki da gaskiya

A jawabinsa shugaban kwamitin ta hannun sakataren kwamitin kuma shugaban sashen aikin gona da albarkar kasa, Ahmed Tijjani ya yi alkawarin yin aiki tukuru domin tabbatar da zaman lafiya a tsakanin bangarorin biyu

Ya kuma bukaci manoma dasu kasance masu bin doka da oda domin tabbatar da zaman lafiya a fadin yankin

Kwamitin ya kunshi sarakuna da shugabannin addinai da manoma da makiyaya

Leave a Reply

%d bloggers like this: