Ku Kiyayi Karbar Na Goro – Kakakin Majalisar Bauchi

0 105

Kakakin majalissar dokokin jihar Bauchi Alhaji Abubakar Sulaiman ya gardadi ma’aikatan jihar akan rashin mutunta ayyukansu da karbar cin hanci da rashawa da kuma kin zuwa aiki.

Suleman ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da ma’aikatan majalisar dokokin jihar a garin Bauchi.

Ya ce sabon tsarin mulkin jihar ba zai amince da rashin da’a bad a kuma sauran batutuwan da za su zubar kimar jihar.

Mataimakin kakakin majalisar Alhaji Lamara Chinade ya bada tabbacin cewa sabuwar gwamnaatin jihar za ta yi aiki tukuru domin ciyar da al’ummar jihar gaba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: