

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Kungiyar malaman fasaha ta kasa (NAAT) ta umurci mambobinta da su fara yajin aikin gargadi na makonni biyu daga yau Litinin
Shugaban kungiyar, Ibeji Nwokoma, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a jiya, ya yi zargin gazawar gwamnatin tarayya wajen aiwatar da yarjejeniyar da suka cimma a 2009.
Ya ce wa’adin kwanaki 14 da suka baiwa gwamnatin tarayya ya riga ya wuce, shiyasa suka tsindima yajin aikin.
Ya kuma ce sunkuma yanke wannan shawarar ne bayan Majalisar Zartaswar kungiyar ta kasa, ta yanke shawarar rufe dukkannin dakunan gwaje-gwaje, wuraren bita, dakunan karatu da kuma gonaki na tsawon lokacin yajin aikin gargadi.
Ya ce kashi 97.8 na rassan kungiyar ne suka kada kuri’ar amincewa da matakin shiga wannan yajin aikin.