Babban hafsan sojin kasa na kasa Laftanal Janar Farouk Yahaya a yau ya bayyana damuwa dangane da karuwar korafe-korafen cin zarafin mata a barikokin soji dake fadin kasarnan.
Faruk Yahaya, wanda ya samu wakilcin kwamandan makarantar kere-kere ta sojin Najeriya, Birigediya Janar Mark Mamman, ya dora alhakin matsalar akan rashin zaman sojoji a gidajensu, inda yace a koda yaushe basa tare da iyalansu.
Yayi jawabi a wajen taron sojin Najeriya mabiya darikar katolika na bana da ake gudanarwa a Makurdin jihar Benue.
Ya nanata cewa babbar matsalar cin zarafin kananan yara shine zata iya haifar da matsalolin da cin zarafin ke jawowa, wadanda a halin yanzu ake fuskanta a yakin da da ake yi da ta’addanci a Arewa maso Gabas.