

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Adadin wadanda suka mutu sanadiyyar wata guguwa mai suna Gombe a kasar Mozambique sun kai 48, kuma hanya daya tilo da ta isa yankin da lamarin ya fi kamari ta lalace.
Guguwar Gombe ta shafi dubun dubatar mutane tun bayan da ta sauka a makon jiya.
Rahotanni sun ce akalla gidaje dubu uku ne suka lalace.
A cewar hukumomi, yankin Mossuril da ke lardin Nampula a arewacin kasar shi ne yankin da lamarin ya fi shafa inda mutane 31 suka mutu.
Har yanzu ba a iya zuwa yankin, sanadiyyar lalacewar hanyoyin mota da na wayar tarho.
Cibiyoyin kiwon lafiya da makarantu da gonakin noma na yankin sun lalace.
Hukumar bayar da agaji ta kasar ta ce za ta taimakawa iyalan da abin ya shafa.