PDP ta kaluballanci Gwamnatin Buhari da ta gaggauta fitowa da kudin makamai

0 69

Jam’iyyar PDP ta kaluballanci Gwamnatin Shugaba Muhammmadu Buhari cewa ta gaggauta fitowa ta yi wa ’yan Najeriya bayanin yadda dal bilyan 3.5 da aka ware domin sayen makamai su ka salwanta, tunda ba a sayo makaman ba.

Haka kuma PDP ta yi kira ga Majalisar Dattawa da Majalisar Tarayya su gaggauta binciken kwakwaf domin gano gaskiyar yadda aka karkatar da kudaden, da kuma wadanda su ka karkatar da su.

PDP ta yi wannan kakkausan kalubale ga gwamnati da kuma kira ga majalisu ne a cikin wata sanarwa da Kakakin Yada Labarai na jam’iyyar, Kola Ologbondiyan ya fitar ga manema labarai a ranar Alhamis.

Jam’iyyar adawar ta ce sabuwar harkallar cuwa-cuwar dala bilyan 2.5 da ake zargin Mashawarcin Buhari kan Harkokin Tsaro, Babagana Monguno na da hannu, wanda shi ma a kwanan baya ya zargi su Buratai sun yi sama-da-fadin dala bilyan 1, sun bayyana cewa babu abin da ke wakana a karkashin gwamnatin Buhari sai masifar jidar makudan kudade.

“Ya kamata Majalisa ta gaggauta gudanar da kwakkwaran binciken gano inda aka karkatar da wadannan makudan kudaden da ya kamata a ce an sayo makamai da su domin a kare rayukan jama’a. Maimakon haka sai zargin karkatar da kudaden ke ta fitowa a karkashin gwamnatin Buhari.

“Irin yadda bangaren tsaron gwamnatin Buhari ke fallasa junan su dangane da zargin karkatar da kudaden makamai, ya nuna yadda ake tseren wuce juna tsakanin manyan jami’an gwamnatin Buhari, su na takarar wanda ya fi wani azurta kan sa da kudaden talakawan da su ka kamata a sayo makamai a kare rayukan su da dukiyoyin su.”

PDP ta ragargaji APC ta da cewa maimakon jam’iyyar ta goyi bayan talakawan kasar nan, sai ta buge da borin-kunyar kokarin kare jami’an gwamnatin da ake zargi sun yi wa junan su watandar kudaden.

Leave a Reply

%d bloggers like this: