Kimanin gidaje 40 ne Gwamnatin jihar Nassarawa tace ta rushe, wadanda aka gina ba bisa ka’ida ba a hanyoyin ruwa, cikin kananan hukumomi 3 jihar.
Haka kuma tace an kama mutane 27, tare da gurfanar dasu a kotun tafi da gidanka, bisa take dokar tsaftar muhalli ta wata wata, da ake wanzarwa a jihar.
A wani labari kuma wata ambaliyar ruwa tayi sanadiyar rushewar kimanin shaguna 6, hadi da wasu gidaje, biyo bayan saukar ruwan sama a jihar.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
- Tsohon sakataren jam’iyyar PDP na kasa ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC
Babban jami’in kula da muhali na ma’aikatar muhalli da albarkatun kasa, Mallam Abubakar Mohammad, shine ya sanar da hakan gay an Jaridu, yayin ziyarar gani da ido, kan yadda shirin tsaftar muhalli ta wata wata ke gudana a Lafia, babban birnin jihar.
Yace gwamnati na daukar matakan ne a kokarin kawo karshen matsalar ambaliyar ruwa a jihar.
Haka kuma yace dabi’ar kunnen kashi da wadansu mutane keyi ga umarnin gwamnati, kan hani da yin gine gine a hanyoyin ruwa, itace ta sanya aka dauki matakin yin rusau.