Kimanin gidaje 40 ne Gwamnatin jihar Nassarawa tace ta rushe, wadanda aka gina ba bisa ka’ida ba a hanyoyin ruwa, cikin kananan hukumomi 3 jihar.
Haka kuma tace an kama mutane 27, tare da gurfanar dasu a kotun tafi da gidanka, bisa take dokar tsaftar muhalli ta wata wata, da ake wanzarwa a jihar.
A wani labari kuma wata ambaliyar ruwa tayi sanadiyar rushewar kimanin shaguna 6, hadi da wasu gidaje, biyo bayan saukar ruwan sama a jihar.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
- Majalisar Zartarwa ta Jigawa ta amince da manyan ayyukan ci gaban lafiyar jihar
Babban jami’in kula da muhali na ma’aikatar muhalli da albarkatun kasa, Mallam Abubakar Mohammad, shine ya sanar da hakan gay an Jaridu, yayin ziyarar gani da ido, kan yadda shirin tsaftar muhalli ta wata wata ke gudana a Lafia, babban birnin jihar.
Yace gwamnati na daukar matakan ne a kokarin kawo karshen matsalar ambaliyar ruwa a jihar.
Haka kuma yace dabi’ar kunnen kashi da wadansu mutane keyi ga umarnin gwamnati, kan hani da yin gine gine a hanyoyin ruwa, itace ta sanya aka dauki matakin yin rusau.