Rikicin kasar Ukraine: ‘Yan Najeriya dake kasar Ukraine ku kula wajen kare kawunaku

0 83

Kasancewar ana cigaba da rikici a kasar Ukraine saboda mamayar kasar Rasha, ofishin jakadancin Najeriaya a Ukraine ya gayawa ‘yan Najeriya dake kasar cewa su kula wajen kare kawunansu.

Mutane da dama sun makale a kasar sanadiyyar rikicin, wanda shugabannin duniya suka kasa shawo kai duk da barazanar takunkumi da magiya.

Ofishin jakadancin ya fadi haka cikin wata shawara da ya fitar jim kadan kafin Rasha ta mamaye Ukraine.

Leave a Reply

%d bloggers like this: