Rundunar ‘yansandan jihar Kebbi ta gabatar da cakin kudi na naira miliyan 60 ga iyalan jami’an ‘yansanda 6 da ‘yan fashin daji suka kashe

0 68

Rundunar ‘yansandan jihar Kebbi a yau ta gabatar da cakin kudi na naira miliyan 60 ga iyalan jami’an ‘yansanda 6 da ‘yan fashin daji suka kashe a bakin aiki.

‘Yansandan sun rasu yayin arangama da ‘yan fashin daji lokacin da suke aikin gadi a kamfanin kayan abinci na GB a kauyen Gafara dake karamar hukumar Ngaski ta jihar ta Kebbi a ranar 15 ga watan Maris.

Kakakin rundunar ‘yansandan, Nafi’u Abubakar, shine ya sanar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar a Birnin Kebbi.

Nafi’u Abubakar yace kwamishinan ‘yansandan jihar, Musa Baba, shine ya mika cakin kudin ga iyalan, a madadin kamfanin na GB.

Kakakin rundunar ‘yansandan ya kuma rawaito kwamishinan na shawarartar iyalan da su yi amfani da kudaden ta hanyar da ta dace wajen farfado da tattalin arzikinsu.

Leave a Reply

%d bloggers like this: