SEMA ta bayyana shirinta na sayen karin kayan agaji domin taimakawa jama’a a lokacin damina – JIGAWA

0 256

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA) ta bayyana shirinta na sayen karin kayan agaji domin taimakawa jama’a a lokacin damina, kamar yadda sabon Sakataren hukumar, Alhaji Hannafi Yakubu Fagam, ya bayyana a wata tattaunawa da akayi da shi a Radio Jigawa a cikin wani shiri mai suna Jigawa A Yau.

Ya ce za’a sayi kayan da suka hada da jarkokin mai, garin fulawa, sukari, kwale-kwale, garin kwari, bargo, tabarma da sauran kayayyakin kariya don rage illar ambaliya.

Hannafi Fagam ya kara da cewa za a horar da ma’aikatan kananan hukumomi don kara fahimtar dabarun daukar matakan gaggawa a lokacin ambaliya. Ya ce hukumar ta rubuta littafi mai dauke da tsare-tsare da matakan kariya daga ambaliya, inda ya kara da cewa hukumar NiMet na hasashen cewa za a samu ruwan sama mai yawa a jihohi da dama, ciki har da jihar Jigawa, musamman a kananan hukumomi kamar Ringim da Taura da Jahun da Miga da Kafin Hausa da Auyo da Hadejia da Kirikasamma da Guri da Malam Madori da kuma Kaugama.

Leave a Reply