

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya zai tafi Belgium a yau Talata don halartar taron haɗin gwiwa tsakanin ƙungiyar haɗin kan Afirka ta African Union (AU) da takwararta ta Tarayyar Turai (EU).
Taron wanda zai gudana a birnin Brussels daga 17 zuwa 18 na Fabarairu, inda shugabannin nahiyoyin biyu za su tattauna matsalolin da ke faruwa a yankunansu.
Wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa ta ce ana sa ran Buhari zai koma gida ranar Asabar. Ta ƙara da cewa shugaban zai yi amfani da damar wajen tattauna sauran al’amura da wasu ƙasashe.
Abubuwan da shugabannin za su tattauna sun haɗa da batun ilimi da sauyin yanayi da makamashi da zaman lafiya da harkokin mulki da harkokin tattalin arziki.