

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa Sule Lamido ya ce yan Najeriya a yanzu haka suna kallon Jam’iyar PDP a matsayin Mafita ga kasar.
Da yake jawabi ga Gidan Talabijin na Channels Tv, a jiya, tsohon Gwamnan ya ce shirye-shiryen da Jam’iyar take yi a yanzu domin karbar ragamar Mulki tana yi domin cigaban yan kasa.
A cewarsa, tuntubar da magoya bayan Jam’iyar suke yi a yanzu haka a sassan kasar, zai kara farfado da jam’iyar.
Tuni wasu masu shaa’war tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyar sunyi nisa da fara tuntuba.
Gwamnan Jihar Rivers Nyesom Wike, ya gana da masu ruwa da tsaki na Jam’iyar PDP a Jihar Neja, inda ya bayyana cewa babu laifi a yin hakan.