

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja.
Shugaban kwamitin zaben Lawrence Ewhrudjakpo ne ya sanar da hakan a sakateriyar jam’iyyar PDP ta jihar, wajen da ake gudanar da zaben fidda gwani a Minna babban birnin jihar..
An ce an kashe wakilan ne a jiya yayin da suke komawa Mariga bayan da jam’iyyar ta dage zaben fidda gwanin sakamakon zanga-zangar da wasu ‘yan takarar suka yi da suka nuna rashin amincewa da jerin sunayen wakilan.
Daga nan aka bukaci wakilan da su kawo katin tantance sunayensu don tantance su.
An sauya wadanda suka rasa rayukansu a lamarin domin cika adadin wakilan karamar hukumar.
Sai dai, daya daga cikin wakilan, Shehu Haruna ya shaidawa manema labarai cewa lamarin ya faru ne a tsakanin Mariga da Tegina kuma mutane hudu sun rasa rayukansu.