Yadda akai dambarwa yayin tsige kakakin majalissar jihar Imo

0 84

‘Yan majalisar jihar Imo sun tsige kakakin majalisar Paul Emeziem a zaman da majalisar ta yi a yau.

‘Yan majalisa 19 ne suka tsige shugaban majalisar daga cikin ‘yan majalisar jihar 27.

A cikin takardar da aka karanta a zauren majalisar, ‘yan majalisar sun ce sun tsige Emeziem ne bisa zarge-zargen da suka hada da nuna rashin da’a da cin mutuncin ofishinsa da kuma babakere da kudaden jama’a.

‘Yan majalisar sun kuma zabi sabon kakakin majalisa Honarabul Kennedy Ibe.

A makon da ya gabata ne, Emeziem ya sanar da tsige makataimakin kakakin majalisar, Amarachi Iwanyanwu.

Bai kuma sanar da dalilin tsigewar ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: