

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz Yari a yau ya fara rabon shanu 400 ga magoya bayansa a kananan hukumomi 14 da mazabu 147 na jihar.
Haka kuma daga cikin wadanda za su ci gajiyar tallafin na bukukuwan Sallah akwai marasa galihu a cikin al’umma.
Shugaban kungiyar Abdulaziz Yari, Lawal Liman, ya mika wasu daga cikin shanun ga wadanda suka amfana yau a Gusau.
Ya lissafa wadanda suka ci gajiyar tallafin da suka hada da malaman addinin musulunci da kungiyoyin matasa da mata da tsofaffi da kuma shugabannin al’umma a jihar.
Ya yabawa tsohon gwamnan bisa yadda yake nuna damuwarsa ga al’ummar jihar musamman marasa karfi.
Lawan Liman ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su samu lokaci a cikin watan Ramadan domin yin addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da ma Najeriya baki daya.