Yau ake cika shekaru 2 da hambarar da mulkin shugaba Omar al-Bashir na shekaru 30 a Sudan

0 88

Yau ake cika shekaru biyu da kadawar guguwar sauyin da ta hambarar da mulkin shugaba Omar al-Bashir na shekaru 30, ana kuma sa ran za a gudanar da zanga-zanga a babban birnin kasar Khartoum.

Gwamnatin riko ta gabatar da tsauraran sauye-sauyen farfado da tattalin arzikin kasar, sannan ta yi nasarar samun farin jini daga kasashen waje.

Sai dai wakilin BBC ya ce tashin farashin kayayyaki, da janye tallafin mai ya sanya yawancin ‘yan kasar cikin mawuyacin hali.

Leave a Reply

%d bloggers like this: