

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Mai Martaba Sarkin Kazaure Alhaji Dr Najib Hussaini Adamu, ya karbi Bakuncin Dan Takarar Gwamnan Jihar Jigawa a karkashin tutar Jam’iyar PDP Alhaji Mustapha Sule Lamido, wanda ake kira Santuraki a fadarsa.
Ziyarar tamkar wasu hanyoyin tuntuba da neman Albarkar masu sarautar gargajiya da masu ruwa da tsakin Jihar Jigawa ne.
An bada rahotan cewa ziyarar ta samu karbuwa da kuma tagomashi daga wuraren masu sarautun gargajiya.
Da yake Jawabi, Mustapha Sule Lamido, ya bawa Sarkin tabbacin cewa Jam’iyar PDP zata gudanar da gangamin yakin neman zaben ta, cikin Ladabi, da mutumta Jama’a.
A cewar Mustapha Sule Lamido, zaiyi aiki tare da masu Sarautun Gargajiya wajen ciyar da Jihar Jigawa gaba, matukar an zabe shi Gwamnan Jiha a shekarar 2023.
Da yake mayar da Jawabi, Mai Martaba Sarkin Kazaure Alhaji Najib Hussaini Adamu, ya bukaci mutane su kasance masu Jin tsoron Allah, da kuma kiyayewa da Dokokin sa, tare da daukar kansu a matsayin yan uwa.