Ƙungiyar Amnesty International ta nemi a dakatar da kamfanin Shell daga hakar mai a yankin Neja Delta

0 72

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Amnesty International ta shiga sahun masu kira ga gwamnatin tarayya da ta dakatar da kamfanin mai na Shell daga gudanar da aikinsa a ƙasar har sai an samar da kariya ga mutanen Neja Delta. Ƙungiyar ta ce ayyukan kamfanin na ƙara haifar da cin zarafin ɗan adam idan har ba a shawo kan matsalar gurɓata muhalli da kamfanin ke haifarwa ba. Ƙungiyar ta ce dole ne kamfanin ya samar da wadatattun kuɗin da za a yi amfani da su wajen gyara gurɓacewar muhalli da ayyukansa ya janyo sannan dole a tuntuɓi mutanen yankin kan maganar sayar da kamfanin kan fiye da dala biliyan 2.4. Masu fafutuka sun zargi Shell da hannu wajen yawan malalar mai a yankin Neja Delta da wasu matsalolin da suka janyo gurbacewar magudanan ruwa. Gwamnatin tarayya dai ba ta ce komai ba kan batun. A baya kamfanin na Shell, ya yi alƙawarin sabbin mamallaka kamfanin za su duba ɓarnar da aka yi.

Leave a Reply

%d bloggers like this: