- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Shugaban kasar Mozambique Filipe Nyusi ya kori ministoci shida da suka hada da ministan kudi a wani gagarumin sauyi cikin wata sanarwa da ofishin shugaban kasar ya fitar.
Sanarwar ba ta bayar da wani dalili na korar ministocin ba, bata kuma nuna alamun lokacin da za a nada sabbi ba.
Wannan dai shi ne babban garanbawul na biyu a fasalin majalisar ministocin a watannin baya-bayan nan.
Sauran da aka kora sun hada da ministan albarkatun ma’adinai da makamashi, da ministan kamun kifi, da kuma na ruwa da ayyukan jama’a, da kuma ministan gidaje da albarkatun ruwa.
Masu lura da harkokin siyasa a kasar sun ce ba su yi mamakin korar da aka yiwa ministocin ba.
A watan Nuwamba, shugaba Nyusi ya kori ministocin tsaro da na harkokin cikin gida tare da maye gurbinsu.