- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Akalla mayakan Boko Haram da na ISWAP dubu 7 ne suka mika wuya ga sojojin Najeriya a makon da ya gabata.
Kwamandan Operation Hadin Kai, Christopher Musa, shine ya sanar da haka a yau yayin wata ganawa da kamfanin dillancin labarai na kasa a Maiduguri.
Christopher Musa yace fatattakar da sojoji ke yiwa mayakan ISWAP da na Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas na cigaba da haifar da da mai ido.
Christopher Musa yayi bayanin cewa ana sa ran sojojin Najeriya da sauran masu ruwa da tsaki zasu tantance mayakan da suka mika kai tare da iyalansu kafin a sauya musu rayuwa.
Kwamandan yace sojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro za su cigaba da lalubo hanyoyi kawo karshen ta’addancin Boko Haram cikin gaggawa.