

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Hukumar Kare Hakkin Mai Saye ta Jihar Kano ta ce ta gano wani wuri da ake sarrafa gurbataccen man girki.
Gano man na daga cikin kokarin da hukumar ke yi na kare jama’a daga amfani da kayayyakin da ba su da kyau da na jabu da kuma gurbatattun kayayyaki.
Manajan Daraktan Hukumar, Idris Bello-Danbazau, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai jiya ta hannun mai magana da yawun hukumar, Musbahu Yakasai, a Kano.
Bello-Danbazau, wanda babban mataimaki na musamman ga gwamna kan harkokin tabbatar da inganci, Honorabul Sale Muhammad, ya wakilta ya jagoranci tawagar bincike zuwa wajen da ke Dakata Rinji a karamar hukumar Nasarawa a cikin birnin Kano.
A cewarsa, wajen sarrafa man girkin yana kusa da wata babbar cibiyar tattara shara.
Ya bayyana cewa wajen ba shi da tsafta kuma yana da hadari ga lafiyar jama’a.