Gwamnan jihar Jigawa Muhammad Baduru Abubakar ya rantsar da sabon babban Khadin Jihar tare da karin wasu alƙalan manyan kotuna a fadar gwamnatin jihar a jiya.
Da yake magana a wurin taron da aka yi shi ba tare da cikowar jama’a ba saboda halin da ake ciki na bukatar karancin cunkoso da bayar da tazara, Gwamna Badaru bukaci sabbin masu Shari’ar da su ji tsoron Allah yayin da suke aiwatar da aikin su.
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2020/05/4DEDBAC1-EE15-4259-A99E-ADF86A5FABBD.jpeg?resize=960%2C639&ssl=1)
Kwamishinan Shari’a na jihar Dr. Musa Adamu Aliyu ne ya jagoranci rantsuwar sabbin alƙalan biyu da kuma babban Khadin.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Alƙalan manyan kotunan su ne mai shari’a Musa Ubale da mai shari’a Husseina Aliyu Adamu sai kuma Khadi Muhammad Sani Salihu.
![](https://www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2020/05/D243D388-F145-4027-A17C-97929D07FCB9.jpeg)
Taron rantsuwa ya samu halartar mataimakin gwamna Malam Umar Namadi da kakakin majalisar dokoki ta jihar Alhaji Adamu Abdulkadir Fanini.
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2020/05/C4BB0346-D398-4BB9-8312-AFF53AD64BE4.jpeg?resize=960%2C639&ssl=1)