

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Ana zargin kwamdan hisbah na Jahar Sheikh Haruna Ibn Sina da karkatar da kujerun hajjin bana ga yan uwan da makusantan sa, da kuma karbar na goro daga wasu jami’an gwamnati domin zuwa kasa mai tsarki.
Rabiu Baba Usman, mai taimakawa gwamna Abdullahi Ganduje kan hukumar hisbah, yace an maye Gurbin sunan sa ba bisa ka’ida ba da sunan matar kwamandan hisba da dan uwan sa a kujerun hajjin da gwamnatin Jahar ta bada, duk da cewa shirye-shiryen tafiyar a ofishin sa yake.
Da farko dai mai taiwakawa gwamnan yace kwamandan hisban ya rubuta sunan sa a matsayin wadanda zasuyi aikin hajjin bana amma daga baya ya cire sunan sa ya maye dana matar sa da dan uwan sa.