

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Asusun horas da ma’aikata na kasa ITF ya horas da matasa 100 a jihar Jigawa sanao’i’n girke-girke da tsara bukukuwa da koyan aikin ruwan famfo.
Babban daraktan asusun, Joseph Ari, shine ya sanar da hakan a lokacin bikin rufe aikin bayar da horan a Dutse, Babban birnin jiha.
Yace matasan da aka zabo daga kananan hukumomin jiharnan 27 sun sami horan ne na tsawon watanni uku.
Joseph Ari wanda ya samu wakilcin Even Okiricha yace an horas da ‘yan Nigeria dubu 3 da 905 sana’o’in girke-girke da tsara bukukuwa, da koyan aikin ruwan famfo, tare da basu jari.
Ya roki gwamnatocin jihohi da kungiyoyi masu zaman kansu da yan siyasa da masu ruwa da tsaki dasu hada gwiwa da asusun a kokarin da yake na samarwa da al’umma sana’o’in dogaro da kai.