

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
A wani labarin makamancin wannan, daliban makarantun sakandare na gwamnati na jihohin Sokoto da Zamfara ba za su rubuta jarrabawar kammala sakandare ta yammacin Afirka (WAEC) ta watan Mayu da Yunin bana.
Shugaban ofishin hukumar jarabawar yammacin Afrika ta kasa (WAEC), Patrick Areghan, wanda ya bayyana hakan a jiya, bai bayyana dalilan matakin ba.
Amma an bayyana cewa hukumar jarabawar ta ki karbar dalibai daga jihar Zamfara bisa wasu basussuka da ake bin jihar tsawon shekaru.
Majiya mai tushe ta tabbatar da yadda gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Abdulaziz Yari, ta ki biyan hukumar jarabawar kudaden daliban da suka dauki nauyin jarrabawar.
Sai dai wannan shi ne karo na biyu da daliban jihar Sokoto na makarantun gwamnati ba za su rubuta jarrabawar ba, kasancewar gwamnati ta gaza gabatar da dalibai a bara.