

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Yan bindiga sun kashe mutane 3 a garin Gurbin Magarya na karamar hukumar Jibia ta Jihar Katsina, tare da raunata mutum 3.
An bada rahotan cewa yan bindigar sun kashe dabbobi 3 a lokacin da suka kaiwa garin hari.
Manema Labarai sun rawaito cewa yan bindigar sun kaiwa garin hari ne da Misalin karfe 10 na Dare a lokacin da mutane suke Bacci.
Wani mazaunin garin Jibia mai suna Halliru Haladu, ya fadawa manema labarai cewa sun kai harin ne akan Babura.
An bada sunayen mutanen da aka kashe da Muntari Naqawuri, da Surajo Salisu da Musa Hassan.
Kawo yanzu, kakakin rundunar yan sandan Jihar Katsina SP Gambo Isah, bai amsa kiran wayar da aka masa ba.