- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Babban banikin kasa CBN yace ya ware sama da naira biliyan 42 domin bunkasa noman alkama a kadada dubu 132, da 799 a jihohi 15 dake fadin kasar nan.
Wannan na kunshe cikin jawabin da gwamnan babban bankin Godwin Emefiele ya yi a wajen bikin kaddamar da shirin girbin alkama daya gudana a kauyen Gabarin na karamar hakumar Ringim a nan jihar jigawa.
Emefiele wanda ya samu wakilcin Hajiya Sa’adatu Ibrahim, babbar mai kula da babban bankin rashen jihar Jigawa, ta bayyana cewa wannan kokari da babban bankin keyi zai kawo karshen kalubalen karanci da hauhawar farashin alkama da ake samu.
Ya bayanin cewa an kirkiri dabarar ne da nufin bunkasa samar da alkama mai kyau ta hanyar amfani da irin alkama da kasashen waje.
a karshen shekarar data gabata ne babban bankin ya kaddamar da rabon kayan aikin noman alkama a kauyen kacallari dake yankin karamar hakumar Malam Madori, kayayyakin da suka hada irin noma, taki, maganin feshi da injin bayi ga monoma.