

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Adamu, yace jam’iyyar bata danasanin sanya naira miliyan 100 a matsayin kudin sayen Fom din, nuna sha’awar tsayawa takarar shugabanci kasa a zaben 2023.
Abdullahi Adamu, ya bayyana hakan ne a juma’a, a fadar shugaban kasa dake babban birnin tarayya Abuja, bayan ya gabatar da dan takarar gwamnan jihar Ekiti a tutar jam’iyyar APC Abiodun Oyebanji ga shugaban kasa Muhammadu Buhari.
A cewarsa sun sanya kudin Fom din ne domin kashe gwaiwar wadanda bada gaske suke ba, domin kuma jam’iyyar ta samu wadataccen kudin da zata shiga babban zaben 2023.
Ya kara da cewa sanya Naira miliyan 100 a matsayin kudin Fom, zai kara kashe gwaiwar jam’iyyun adawa, domin APC ta samu nasara a zaben 2023.