

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Jigo a jam’iyyar APC kuma tsohon gwamnan jihar Legas Bola Tinubu, ya sayi Fom din nuna sha’awar tsayawa takara a jam’iyyar APC, bayan ya biya Naira miliyan 100 a yau Juma’a.
Manema labarai sun gano cewa Tunubu, wanda yanzu haka yake kasar Saudi Arabia, wasu na hannun daman sa ne suka jagoranci sayo masa Fom din.
Wadanda suka hada da dan majalissar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Agege dake jihar Legas James Faleke, Sanata Babatunde Adejare, sai kuma tsohon sakataren gwamnatin tarayya Babachir Lawal.
Kafin hakan dai Tunubu ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar ne a watan Mayu bana, bayan ya kammala ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Tunubu ya kasance mutum na uku a halin yanzu daya mallaki Fom din tsayawa takarar shugabancin kasa a jam’iyyar APC, bayan karamin ministan Ilimi Emeka Nwajiuba da kuma gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello.