

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 2 ga watan Mayu da kuma Talata 3 ga watan Mayu a matsayin ranakun hutun Sallah ta bana da kuma ranar ma’aikata ta bana.
Ministan harkokin cikin gida Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan a jiya, amadadin gwamnatin tarayya.
Ya kuma taya ma’aikata dake fadin kasar nan murnar, bisa irin namijin kokarin sukeyi wajan gudanar da ayyukansu.
Ya kara da cewa kwazon aikin sune yasa kasar nan take samun nasarori a kowanne bangare, tare da daga likafar kasar nan a idon duniya.
Ministan ya kuma bukaci musulmai da suyi amfani da bikin Sallar, wajan yin adduar zaman lafiya tare da adduar Allah ya albarkaci Nijeriya.