

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Gwamnatin Tarayya tace baza a bude miliyoyin layukan waya da aka rufe makon da ya gabata ba, har sai masu layukan sun hada layukan da lambar shaidar zama dan kasa ta NIN.
An sanar da haka cikin wata sanarwa a yau daga hukumar sadarwa ta kasa (NCC).
Hukumar tace sanarwar ta zama tilas bisa yadda aka samu wani shafin internet da ake yadawa a kafafen sada zumunta da wasu shafunkan internet.
Hukumar tace shafin na dauke da labarai da bayanan karya da aka kirkira da nufin yaudarar mutane akan layukan da aka hada kiran waya, saboda rashin hada su da lambobin NIN.
Kazalika, hukumar ta NCC tace masu layukan wayan da basu da lambobin NIN, akwai bukatar suje ayi musu rijistar layi a cibiyoyin da aka ware a kasarnan, daga nan sai su hada layin da lambar NIN ta hanyoyin da kamfanonin layin waya suka bayar.