Cutar Lassa ta kashe mutum 92 a Najeriya

0 67

Cibiyar dakile bazuwar cututtuka takasa NCDC ta ce adadin mutanen da cutar Lassa ta kashe a 2021 a kasar nan sun kai 92.

Cutar Lassa wacca ake kamuwa da ita daga abincin da bera yayi mu’amala da shi, ko kuma yin mu’amala da mutumin dake dauke da wannan cutar, tanada alamun da suka hada da ciwon kai, Amai, Gudawa, ciwon makogoro, ciwon kirji, ciwon gabobi, kasala, tari da kuma  zazzabi, haka kuma tana sanya yoyon idanu, hanci, da kuma zubar da yawu a baki.

Leave a Reply

%d bloggers like this: