

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Fadar shugaban kasa ta nisanta shugaban kasa Muhammadu Buhari da shirin tsayar da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a matsayin dan takarar jam’iyyar APC.
Majiyoyin fadar shugaban kasar sun bayyana hakanne a karshen makon jiya, inda sukace shugaba Buhari, wanda ya bayyana jam’iyyar PDP a matsayin marar nasara a wata hira da yayi da wani gidan talabijin.
Buhari ba zai iya goyon bayan duk wani yunkuri na tsaida toshon shugaban kasa Jonathan a matsayin dan takarar shugabancin kasa a zaben 2023 ba.
Wannan na zuwa ne bayan, an zargi guda cikin hadiman shugaban kasa Buhari, da saka photunan Jonathan a gaba-gaba, dake nuni da cewa, watakila Buhari ya goyi bayan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.
Amma, Fadar shugaban kasar ta kara tabbatar da cewa, shugaban kasa Muhammadu Buhari bai bayyana wanda yake marawa baya ba a zaben fidda gwani na shugaban kasa a tutar jam’iyyar APC ba.
Sai dai an yi ta rade-radin cewa Jonathan ne akafi ganin cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari zai marawa baya.