

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Fadar shugaban kasa tace jam’iyyar PDP mai adawa za ta mutu kamar yadda daya daga cikin ‘yan takararta na shugaban kasa yayi hasashe, muddin fatan da take yiwa kasarnan shine gudanar da zanga-zanga akan halin da ake ciki, wacce tafi ta EndSARS muni.
Mai bawa shugaban kasa shawara na musamman akan kafafen yada labarai, Femi Adesina, shine ya sanar da haka cikin wata sanarwa jiya a Abuja.
Ya bukaci PDP da ta mayar da hankali wajen hada kan kasarnan akan take tunanin barkewar zanga-zangar da tafi EndSARS muni, wacce aka samu asarar rayuka da tashe-tashen hankula.
Yace jam’iyyar PDP ta badawa kanta kasa a fuska yadda ta nuna cewa burinta kawai shine wanzar da rikici a kasarnan domin samun damar komawa karagar mulki.