

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Hukumar Hisbah ta jihar Jigawa ta sanar da kama mutane 99 a kananan hukumomin Kazaure da Dutse bisa laifin aikata badala.
Kwamandan Hisbah na jiha, Mallam Ibrahim Dahiru, wanda ya zanta da manema labarai yau a Dutse, yace wadanda aka kama da suka kunshi mata 54 da maza 44, an kama su ne a ranakun 16 da 17 ga watan Maris a wasu sumame daban-daban da jami’an hukumar suka kaddamar.
Yayi bayanin cewa mutane 91 cikin wadanda aka kama, da suka hada da mata 49 da maza 42, an kama su a ranar 16 ga watan Maris, bayan wani sumame da aka kai Gada Kazaure.
A cewarsa, wadanda aka kama, ana zarginsu da aikata badala tsakanin mata da maza.
Kwamandan yayi bayanin cewa ragowar mutane 8 da aka kama da suka hada da mata 5 da maza uku, an kama su a ranar 17 ga watan Maris a Dutse.
Ya kara da cewa an kwace kwalabe 8 na giya a lokacin sumamen.