Bayan kwashe shekaru yana aikin koyarwa a Jami’ar Bayero dake Kano, babban limamin masallacin birnin tarayya dake Abuja Farfesa Ibrahim Ahmad Said Maqariy (Hafizahulla) ya ajiye aikinsa domin maida hankali wajen hidimtawa Addini.
Bayan Jami’ar ta Bayero ta amince da ajiye aikin malamin, a wata takarda dake dauke da amincewar hukumar makarantar.
Malam Maqarin ya bayyana cewa ya dauki wannan matakin ne domin yana daya daga cikin mafarkinsa tun bai wuce Shekara Ashirin ba,yake fatan ya daina aikin gwamnati.
- Sanata Shehu Buba zai horas da matasa 250 kan sana’ar gyaran takalma a jihar Bauchi
- Cibiyoyin kula da lafiyar kafafu da hannaye a Najeriya ta bude sabon ofishi a Kano
- Gwamnan Namadi ya amince da Mai Martaba Sarkin Kazaure a matsayin Amirul Hajj na jihar Jigawa
- Dalibai 41,000 da ba su kai shekara 16 ba sun yi rajistar JAMB ta shekarar 2025
- Za a fara gudanar da jarrabawar WAEC da NECO ta hanyar na’ura wato CBT
Sai a wannan Shekarun Allah Ya karbeshi a matsayin Mai cikakken yiwa addini hidima da Ma’aikatan Addini.
Inda ya kara da cewa Koda yake kowa da yanda Allah Ya tsara masa rayuwarsa, ba ya nufin wadanda ba haka ba ya fisu.
Maqari “Alhamdulillah da na bar Aikin Albashi da Kaina da Qarfina. Allah Ya Albarkaci abinda zai biyo baya na”