Bayan kwashe shekaru yana aikin koyarwa a Jami’ar Bayero dake Kano, babban limamin masallacin birnin tarayya dake Abuja Farfesa Ibrahim Ahmad Said Maqariy (Hafizahulla) ya ajiye aikinsa domin maida hankali wajen hidimtawa Addini.
Bayan Jami’ar ta Bayero ta amince da ajiye aikin malamin, a wata takarda dake dauke da amincewar hukumar makarantar.
Malam Maqarin ya bayyana cewa ya dauki wannan matakin ne domin yana daya daga cikin mafarkinsa tun bai wuce Shekara Ashirin ba,yake fatan ya daina aikin gwamnati.
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
- EFCC sun kai samame gidan tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello da ke Abuja
- Kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP a Najeriya ya bayyana goyon bayansa ga Umar Damagum
- MƊD za ta ƙaddamar da asusun neman taimako domin samar da kayan agaji ga Falasɗinawa a Gaza
- Gwamnan Jihar Jigawa ya nemi ma’aikatun jihar da su cimma yarjejjeniyar da jihar ta kulla da Ofishin FCDO
Sai a wannan Shekarun Allah Ya karbeshi a matsayin Mai cikakken yiwa addini hidima da Ma’aikatan Addini.
Inda ya kara da cewa Koda yake kowa da yanda Allah Ya tsara masa rayuwarsa, ba ya nufin wadanda ba haka ba ya fisu.
Maqari “Alhamdulillah da na bar Aikin Albashi da Kaina da Qarfina. Allah Ya Albarkaci abinda zai biyo baya na”