Mai girma Gwamnan Jihar Jigawa ya umarchi maikatrar Lafiya karkashin kwaminshinan Lafiya Dr. Abba Zakari Umar dasu tantance yara 60 Yan asalin jihar Jigawa masu sha’awar karatun likita wato medicine domin gwamnati ta dauki nauyin su zuwa karatu kasar waje.
Za a dauki yara biyu daga kowacce mazabar dan majalissa.
Ana bukatar yara Yan kasa da 23, wadanda suke da a kalla credit 5 a Biology, Chemistry, Physics, English da mathematics.
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
- Gwamnati na shirin farfado da masaku da nufin bunkasa noman auduga da samar da tufafi
- Hukumomi na aiki da jami’an tsaro wajen kamo duka ragowar fursunoni 109 da suka tsere daga gidan gyaran hali
- Za’a gudanar da cikakken bincike don tabbatar da ingancin duka jiragen sama da ke zirga-zirga a Najeriya
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
Wannan shiri na yayan talakawa ne kawai wadanda suka gama karatun secondary a makarantun gwamnati kuma za a zakulo yaran bisa chancanta kawai.
Ana bukatar daukar a kalla mata 30, maza 30.
Duk me sha’awa yakai takardunsa ofishin kwamishinan lafiya na Jigawa Dr. Abba Zakari Umar daga ranar Juma’a 3rd July.
Kwamishinan lafiya na jihar Jigawa Dr. Abba Zakari Umar yace za’a rufe karbar takardun ranar 10 ga July a kuma yi jarrabawar tantancewa ranar litinin 13th July 2020.